Ƙungiyoyi masu Goyon Bayan APC 1,500 Sun Mara wa ‘Renewed Hope Network’ Baya Domin Tazarcen Tinubu a 2027

Wasu ƙungiyoyi masu goyon bayan jam’iyyar APC da suka kai 1,500 sun bayyana goyon bayansu ga ƙungiyar Renewed Hope Network (TRN) domin ƙarfafa shirye-shiryen tazarcen Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu a zaɓen shugaban ƙasa na shekarar 2027.
Sanarwar goyon bayan ta fito ne ta hannun Mataimakin Darakta Janar na APC Support Groups Council, AK Peters, a birnin Abuja, inda ya bayyana cewa matakin ya biyo bayan wani muhimmin taro da majalisar ta yi da tawagar fasaha ta ƙungiyar Renewed Hope Network.
A cewarsa, tawagar ta haɗa da gogaggen mai fafutukar siyasar APC kuma tsohon Babban Mataimaki ga Shugaban Jam’iyyar APC kan ƙungiyoyin farar hula da ƙungiyoyin goyon baya, Okpokwu Ogenyi, tare da fitaccen jami’in diflomasiyya na ƙasa da ƙasa Tunji John Asaolu.
Rahoton ya nuna cewa Renewed Hope Network wata manhaja ce ta siyasa da tsohon gwamnan Zamfara kuma Sanata mai wakiltar Zamfara West Senatorial District, Abdulaziz Yari, ke jagoranta, wadda aka kirkiro domin ƙarfafa wayar da kan jama’a da tattara magoya baya a matakin ƙasa gabanin babban zaɓen shugaban ƙasa na 2027.
Sanarwar ta kara da cewa ƙungiyar ta fara aiwatar da wasu muhimman tsare-tsare, ciki har da fara tattara masu yaƙin neman zaɓe a dukkan rumfunan zaɓe da ke faɗin ƙasar nan domin samar da ingantaccen haɗin kai da hulɗa da jama’a a matakin ƙasa.
A cewar AK Peters, jam’iyyar APC na da sama da ƙungiyoyin da suke mara mata baya 3,500 da aka yi wa rajista, inda 1,500 daga cikinsu suka riga suka amince da shiga cikin shirin Renewed Hope Network, yayin da ake sa ran ƙarin 2,000 za su shiga kafin bukukuwan Easter.
Ya bayyana cewa tsarin da ƙungiyar ta kafa da kuma dabarun da ta tsara na da nufin tabbatar da gagarumar nasara ga Shugaba Bola Ahmed Tinubu a zaɓen 2027.
Peters ya kuma jaddada cewa jagorancin da Sanata Abdulaziz Yari ke bayarwa a ƙungiyar Renewed Hope Network zai taka muhimmiyar rawa wajen ƙarfafa haɗin kan magoya bayan jam’iyyar APC da kuma bunƙasa harkokin yaɗa manufofin gwamnatin tarayya a matakin ƙasa.
Ya ƙara da cewa ƙungiyoyin goyon bayan APC sun kuduri aniyar ci gaba da wayar da kan al’umma da tattara goyon baya domin ganin an sake rantsar da Shugaba Bola Ahmed Tinubu karo na biyu a ranar 29 ga Mayu, 2027.




