Labarai

Kwamishinan ‘Yan Sanda na Abuja Ya Umarci ayi Gwajin Kwakwalwa ga Jami’ai dake aikin a Birnin

Kwamishinan ‘yan sanda na babban birnin tarayya Abuja, Ahmed Sanusi, ya bayar da umarnin gudanar da gwajin lafiyar kwakwalwa ga dukkan jami’an rundunar da ke aiki a yankin.

 

 

Wannan mataki na daga cikin kokarin rundunar na kara inganta ladabtarwa, kwarewa da kuma ingancin aiki a tsakanin jami’anta, domin tabbatar da kyakkyawan gudanar da ayyukan tsaro.

 

 

Sanarwar ta fito ne ta bakin jami’ar hulda da jama’a ta rundunar, Josephine Adeh, a ranar Alhamis, inda ta bayyana cewa an dauki wannan mataki ne bayan wani taron gaggawa da ya hada kwamishinoni, kwamandojin yankuna, jami’an yanki da kuma shugabannin rundunonin dabaru.

Related Articles

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Back to top button