Ganduje Ya Yi Martani Kan Zargin Bacewar Dadiyata

Tsohon Gwamnan Jihar Kano, Abdullahi Umar Ganduje, ya yi kakkausar suka tare da yin watsi da zargin da tsohon Gwamnan Jihar Kaduna, Nasir El-Rufai, ya yi masa dangane da bacewar Abubakar Idris, wanda aka fi sani da Dadiyata.
A wata sanarwa da tsohon Kwamishinan Yaɗa Labarai da Harkokin Ciki na Jihar Kano, Muhammad Garba, ya sanya wa hannu, Ganduje ya bayyana zargin a matsayin maras tushe da maras hujja, yana mai cewa an yi shi ne da nufin karkatar da alhakin abin da ya faru a Jihar Kaduna.
Sanarwar ta jaddada cewa Dadiyata ya rayu kuma ya gudanar da ayyukansa ne a Kaduna, inda aka san shi da sukar gwamnatin jihar a wancan lokaci.
A cewar Garba, babu wata hujja da ke nuna cewa Dadiyata ya mayar da hankali kan gwamnatin Kano ko kan Ganduje a lokacin.
Ya kara da cewa alhakin tsaro a wancan lokaci yana karkashin gwamnatin Jihar Kaduna tare da hukumomin tsaron tarayya da ke aiki a can, yana mai cewa “kowa a Kaduna ya san irin sukar da yake yi da kuma inda yake nufi.”
Sanarwar ta bukaci a gudanar da cikakken bincike kan kalaman El-Rufai, tare da jaddada cewa manyan zarge-zarge irin wadannan dole ne su kasance bisa hujjoji, ba maganganun siyasa kawai ba.
Ta kuma bayyana cewa jefa Ganduje cikin lamarin ba tare da shaida ba na iya siyasantar da wani lamari mai sarkakiya da radadi.
Garba ya ce a lokacin mulkin Ganduje na wa’adi biyu a Kano, an ba kafafen yaɗa labarai dama, tare da karbar suka da ra’ayoyin adawa, ba tare da tarihin kama ko gallazawa masu suka ba.
Ya kuma tunatar da cewa tattaunawar jama’a kan bacewar Dadiyata ta fi karkata ne kan abubuwan da suka faru a Kaduna, inda ya ambaci maganganun tsohon Sanata Shehu Sani da kuma mai sharhi Reno Omokri kan batun.
A karshe, Garba ya yi kira ga duk wanda ke da sahihin bayani kan bacewar Dadiyata da ya gabatar da shi ga hukumomin da suka dace, yana mai jaddada cewa dole ne a bi doka da ka’ida domin tabbatar da gaskiya da adalci, tare da gujewa maida lamarin kayan siyasa.




