Gwamna Abba Yusuf Ya Nuna Bacin Rai Kan Halayen Wasu Matasa Bayan Sauya Sheƙa zuwa APC

Gwamnan Jihar Kano, Alhaji Abba Kabir Yusuf, ya bayyana matuƙar bacin ransa tare da nuna damuwa mai tsanani kan halayen rashin da’a da haɗari da wasu matasa suka nuna bayan sun shiga Fadar Gwamnatin Jihar Kano ba bisa ƙa’ida ba, a yayin bikin karɓarsa zuwa jam’iyyar All Progressives Congress (APC).
Gwamnan ya bayyana matsayinsa ne a wani taron masu ruwa da tsaki da ya haɗa shugabannin APC da manyan jami’an gwamnati, inda ya bayyana lamarin a matsayin abin tayar da hankali da ba za a amince da shi ba, yana mai gargaɗin cewa hakan na iya lalata kyakkyawan tarihin Jihar Kano na zaman lafiya, ladabi da bin doka.
A yayin bikin sauya sheƙar, an ruwaito cewa daruruwan matasa sun mamaye harabar Fadar Gwamnatin Kano. Shaidu sun zargi cewa wasu daga cikin matasan, waɗanda ake cewa sun rakiyo Murtala Sule Garo zuwa wajen taron, suna ɗauke da makamai masu haɗari, yayin da wasu kuma suka rika shan miyagun ƙwayoyi a fili tare da yin ihu da kalmar “wuta.”
Haka kuma, an ji wasu na kira da a sauke Mataimakin Gwamna domin a maye gurbinsa da Murtala Sule Garo, wanda aka fi sani da Kwamanda.
Wasu daga cikin al’umma sun dade suna zargin Murtala Sule Garo da yawan tara gungun matasa da ke rakiyarsa zuwa tarukan siyasa, waɗanda ake alaƙanta su da aikata tashin hankali da karya doka.




