Hatsaniya Ta Kaure Yayin Da El-Rufai Ya Je Hedikwatar EFCC a Abuja

An samu hatsaniya tsakanin magoya bayan tsohon gwamnan Jihar Kaduna, Nasiru El-Rufai, da wasu da suka fito domin goyon bayan a bincike shi, a harabar hedikwatar EFCC da ke Abuja.
Lamarin ya faru ne yayin da El-Rufai ya je ofishin hukumar domin amsa gayyata.
Rahotanni sun ce ɓangarorin biyu sun fara cacar baki ne a harabar ginin, lamarin da ya tilasta jami’an tsaro amfani da hayaƙi mai sa hawaye domin tarwatsa masu zanga-zangar.
Bidiyoyin da ‘yan jarida suka ɗauka sun nuna wasu daga cikin waɗanda ke goyon bayan a bincike shi suna rera taken “El-Rufa’i bai fi ƙarfin doka ba” da kuma “a bar doka ta yi aikinta.”
A ɓangaren magoya bayansa kuwa, an ji suna rera taken cewa “za su dawo” duk da hayaƙin da ya lullube yankin.
Ɗaya daga cikin magoya bayansa ya shaida wa BBC cewa sun fusata ne saboda zargin cewa an bari masu adawa da shi sun kusanci kofar ginin suna zaginsa, alhali su ba a ba su damar isa kusa ba.
El-Rufai, wanda ke cikin jagororin adawa na jam’iyyar ADC na shirin ƙalubalantar Shugaban Ƙasa Bola Tinubu na APC a zaɓe mai zuwa.
Tsohon gwamnan ya zargi gwamnati da amfani da binciken rashawa a matsayin hanyar matsin lamba kan ‘yan adawa.
Ya kuma bayyana cewa an riga an kama kusan mutane huɗu da suka yi aiki tare da shi a Jihar Kaduna, yana mai cewa tun da daɗewa yake sa ran za a gayyace shi domin amsa tambayoyi.
A cewarsa, abin da ya faru ya ƙara tabbatar masa da zaton da yake yi cewa lokaci ne kawai ake jira kafin a buƙaci ya bayyana a gaban hukumar.




