Sabon Rahoto Ya Bankado Tsarewa Da Sace ’Yan Jarida 44 A Habasha

Wani sabon rahoto da ƙungiyar tallafa wa kafafen yaɗa labarai ta duniya, International Media Support (IMS) ta fitar, ya nuna cewa aƙalla ’yan jarida 44 ne aka sace ko aka tsare a ƙasar Habasha cikin shekarar 2025.
Rahoton ya bayyana cewa an samu ƙaruwar kai hare-hare kan ’yan jarida, da kamun ba gaira ba dalili, tare da barazanar tara kuɗi ga ma’aikatan kafafen yaɗa labarai da gidajen watsa labarai.
Binciken ya nuna cewa matsin lamba kan kafafen yaɗa labarai ya ci gaba kamar yadda aka gani a shekarar 2024, lokacin da aka daure ’yan jarida 43, lamarin da ke nuna ƙara tabarbarewar yanayin aikin jarida a ƙasar.
Ƙungiyar IMS ta bayyana shekarar 2025 a matsayin lokaci mai matuƙar damuwa ga ’yan jaridar Habasha, sakamakon yawaitar tsare-tsare, sace-sace da muzgunawa da suke fuskanta yayin gudanar da aikinsu.
Rahoton ya kuma yi nuni da irin haɗurran da sassa daban-daban na kafafen watsa labarai ke fuskanta a yanayi mai ƙara zama haɗari, wanda matsalolin siyasa, dokoki, tsaro da kuma tattalin arziki ke haddasawa.
Masu sa ido kan harkokin ’yancin aikin jarida na ci gaba da nuna damuwa kan yadda yanayin ke ƙara tsananta, tare da kira ga hukumomi da su tabbatar da kariya da ’yancin ma’aikatan kafafen yaɗa labarai.




