Dan’agundi Ya Taya Nasir Jao’ji Murnar Nadin Daraktan City Boy Movement a Kano

Baffa Babba Dan’agundi, ya taya Hon. Nasir Bala Aminu Jao’ji (Adon Garin Ƙasar Hausa) murnar nadin da aka yi masa a matsayin Daraktan City Boy Movement a Jihar Kano.
Dan’agundi ya bayyana nadin a matsayin mataki mai muhimmanci kuma na kan lokaci, wanda zai ƙara ƙarfafa harkokin wayar da kan jama’a da haɗa gindin siyasa a matakin ƙasa-ƙasa.
A cewarsa, nadin ya nuna shugabanci mai hangen nesa, inda aka sanya mutumin da ya dace a gurbin da ya dace a wani muhimmin lokaci na tafiyar siyasa.
Ya ce City Boy Movement na buƙatar shugabanci mai nagarta, tsari da kuma ƙarfi a matakin ƙasa-ƙasa, inda ya jaddada cewa Hon.
Nasir Jao’ji na da waɗannan siffofi gaba ɗaya.
Dan’agundi ya kuma bayyana Hon. Jao’ji a matsayin gogaggen mai tara jama’a a matakin ƙasa-ƙasa, tare da bayyana shi a matsayin fitaccen mai taimakon jama’a wanda tasirinsa ya shafi malamai (Ulama), sarakunan gargajiya, maza, mata da matasa a faɗin al’umma.
Dangane da alaƙar siyasa, Dan’agundi ya tabbatar da cikakken goyon bayan Tinubu Support Group ga City Boy Movement, yana mai cewa ƙungiyar za ta ci gaba da marawa shirin Renewed Hope Agenda na Shugaba Bola Ahmed Tinubu baya.
A ƙarshe, Tinubu Support Group a Jihar Kano ta tabbatar wa Hon. Nasir Bala Aminu Jao’ji da cikakken goyon baya da haɗin gwiwa domin tabbatar da nasarar aikinsa a matsayin Daraktan City Boy Movement, tare da bayyana kwarin gwiwar cewa ƙarƙashin jagorancinsa, ƙungiyar za ta faɗaɗa tasirinta tare da ƙarfafa gindin jam’iyyar APC a Kano da ma ƙasa baki ɗaya.



