INEC Ta Sanya Sabbin Ranakun Zaɓen 2027

Hukumar Zaɓe Mai Zaman Kanta ta Najeriya (INEC) ta sanar da sabbin ranakun gudanar da zaɓen shugaban ƙasa, gwamnoni da kuma na ’yan majalisun tarayya da na jihohi na shekarar 2027.
Matakin na zuwa ne mako biyu bayan hukumar ta fitar da jadawalin zaɓen na farko, wanda ya sha suka daga sassa daban-daban na al’umma, sakamakon yiwuwar ranakun su faɗa cikin watan azumin Ramadan na shekarar 2027.
Tun farko, INEC ta sanya ranar 20 ga watan Fabrairu 2027 a matsayin ranar zaɓen shugaban ƙasa da na ’yan majalisar dokokin tarayya, sai kuma 6 ga watan Maris 2027 domin zaɓen gwamnonin jihohi da na ’yan majalisar dokokin jihohi.
Sai dai bayan muhawara da suka taso, lamarin ya kai ga gyaran dokar zaɓe da Majalisar Dokokin ƙasa ta yi, musamman kan mafi ƙarancin lokacin da ya kamata a sanar da ranar gudanar da zaɓe.
A cikin wata sanarwa da hukumar ta fitar ranar Alhamis, 26 ga Fabrairu 2025, mai ɗauke da sa hannun shugaban kwamitin wayar da kan masu kaɗa ƙuri’a, Mohammed Kudu Haruna, INEC ta bayyana cewa bayan gyaran dokar zaɓe ta 2022 da kuma amincewa da sabuwar dokar zaɓe ta 2026, ta sake tsara jadawalin shirye-shiryen zaɓe da ranakun gudanar da su domin su dace da tsarin sabuwar doka.
Hukumar ta ce sauye-sauyen na da nufin tabbatar da bin doka da kuma bai wa dukkan ɓangarori damar yin shiri yadda ya kamata kafin babban zaɓen 2027.




