Labarai
NNPCL ya gargadi mutane su ankare da masu badda kama da sunan wakilan Kamfanin suna karbar kudade a hannun jama’a

Kamfanin Man Fetur na Nijeriya NNPCL ya fitar da sanarwar gargadi ga jama’a da kamfanoni da su yi hattara da ‘yan damfara da ke ikirarin wakilan kamfanin ne.
Babban jami’in yada labaran kamfanin NNPCL Olufemi Soneye, ya sanar a ranar Litinin ya bayyana cewa wadannan ‘yan damfara suna neman kudi a hannun mutane da sunan NNPC don haka jama’a da kamfanonu su yi taka tsan-tsan da irin wa’yannan mutane.




