Labarai
Tsohon Gwamnan Jihar Benuwe, Samuel Ortom, ya ce bai taɓa tsanar marigayi Shugaba Muhammadu Buhari ba.

Ya bayyana cewa ya yi suka ne kawai saboda gwamnatin Buhari ba ta ɗauki matakin da ya dace kan matsalar tsaro da ke addabar jiharsa a lokacin.
Ortom ya ƙara da cewa da gwamnatin Buhari ta karɓi shawararsa kuma ta yi aiki da ita, da matsalar tsaro a Benuwe ta ƙare.
Yayin da yake magana a shirin Politics Today na gidan talabijin na Channels a ranar Litinin, Ortom ya ce dole ya fito ya faɗi gaskiya domin kare rayukan mutanen da yake wakilta.
Ya ce ya dinga ƙorafi ne domin gwamnatin Buhari ba ta ɗauki matakin da ya dace ba game da kashe-kashen da ake yi a Benuwe.




