Labarai

Najeriya Ta Fuskanci Sake Katsewar Wutar Lantarki Sakamakon Lalacewar Babban Layi

Najeriya ta sake fuskantar katsewar wutar lantarki sakamakon lalacewar babban layin wutar lantarki na ƙasar, a ranar Talata.

Wannan shi ne karo na biyu a shekarar 2026 da babban layin ke fuskantar irin wannan matsala, wadda ta haifar da katsewar wuta a sassa da dama na ƙasar.

Lalacewar layin ta fara ne tun a ranar Juma’a da ta gabata.

Masana da hukumomi sun danganta matsalar ne da tangarɗar na’urori da rashin cikakken gyare-gyare da kulawa ga manyan layukan wuta.

Bincike ya nuna cewa dukkanin tashoshin samar da wutar lantarki 23 da ke haɗe da babban layin sun daina aiki gaba ɗaya.

A halin yanzu, babu cikakken bayani kan abin da ya janyo wannan lalacewa, sai dai hukumomi sun fara gudanar da bincike domin gano musabbabin matsalar da kuma daukar matakan gyara.

Related Articles

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Back to top button