Labarai

Gwamnatin jihar Katsina ta ce masu tsegunta wa ƴanbindiga bayanai ne ke haddasa kashi 80 cikin 100 na hare-haren yanbindiga a faɗin jihar.

Kwamishinan tsaro da al’amuran cikin gida na jihar, Nasir Mua’azu ne ya bayyana haka yayin da yake jawabi ga manema labarai a jihar.

Nasir Mu’azu ya ce masu kwarmata wa ƴanbindigar bayanai da ke kai musu abinci da sauran abubuwa ne ke ba su bayanan da suke buƙata domin ƙaddamar da hare-hare.

Kwamishinan ya ce hakan kuma na matuƙar kawo wa gwamnati tsaiko wajen yaƙi da matsalar ƴan fashin daji a faɗin jihar.

Ya ƙara da cewa wasu daga cikin irin waɗannan mutane kan kai wa ƴanbindigar abubuwan da suke buƙata har dazuka su kuma sayar musu a farashi mai tsada.

Kwamishinan ya yi zargin cewa wasu ma daga ciki kan haɗa baki da ƴanbindigar wajen sace mutanen da suke so a sace ciki kuwa har da danginsu.

Related Articles

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Back to top button