Labarai
Fiye da ‘Yan Bindiga 150 ne Suka Halaka ‘a Hatsarin jirgin Ruwa a Sokoto

Rahotanni sun bayyana cewa lamarin ya faru ne a yammacin ranar Asabar, lokacin da ‘yan bindigar ke ƙoƙarin ketare wani ruwa domin isa wani wuri.
Majiyoyin cikin gida sun shaida cewa kwale-kwalen, wanda ake zargin yana ɗauke da ɗimbin ‘yan bindiga, ya kife ne a tsakiyar tafiya, lamarin da ya janyo nutsuwar da dama daga cikinsu
Wasu daga cikin waɗanda ke cikin kwale-kwalen sun yi ƙoƙarin ceto kansu ta hanyar iyo, amma rahotannin farko na nuni da cewa babu wanda ya tsira daga cikin waɗanda hatsarin ya rutsa da su.
Sai dai, har zuwa lokacin haɗa wannan rahoto, babu wata sanarwa a hukumance daga jami’an tsaro da ta tabbatar da yawan waɗanda suka mutu ko cikakken bayani kan lamarin.



