Siyasa

Gwamna Abba Kabir Yusuf Ya Fice daga Jam’iyyar NNPP

Gwamnan Jihar Kano, Alhaji Abba Kabir Yusuf, ya sanar da ficewarsa daga jam’iyyar New Nigeria People’s Party (NNPP) a hukumance, sakamakon tsananin rikice-rikicen cikin gida da kuma buƙatar kare muradun al’ummar Jihar Kano.

 

 

Sanarwar murabus ɗin na ƙunshe ne cikin wata takarda da mai magana da yawun Gwamnan, Sunusi Bature Dawakin Tofa, ya sanya wa hannu a ranar Juma’a. A cikin takardar, Gwamnan ya bayyana cewa ya janye daga jam’iyyar ne tun daga ranar Juma’a 23 ga Janairu, 2026.

 

 

Gwamna Yusuf ya aike da wasiƙar murabus ɗinsa zuwa ga Shugaban Jam’iyyar NNPP na Mazabar Diso-Chiranchi, da ke Ƙaramar Hukumar Gwale, inda ya gode wa jam’iyyar bisa damar da ta ba shi da kuma goyon bayan da ya samu tun farkon shigarsa siyasa a ƙarƙashin inuwarta.

 

 

A cikin wasiƙar, Gwamnan ya bayyana cewa rikice-rikicen cikin gida da ƙalubalen shari’a da ke addabar jam’iyyar a faɗin ƙasar nan sun haifar da rabuwar kai da raunana haɗin kai a tsakanin mambobinta.

 

 

Ya ce ya ɗauki wannan mataki ne bayan yin tunanin zurfi, tare da jaddada cewa shawarar ta dogara ne kacokam kan muradun jama’a. Gwamnan ya bayyana cewa murabus ɗinsa bai samo asali daga wata ɓacin rai ba, illa don ganin an samu kwanciyar hankali da ci gaba mai ɗorewa a Jihar Kano.

 

 

An kuma ruwaito cewa Gwamnan ya fice daga jam’iyyar ne tare da ’yan Majalisar Dokokin Jihar 21, ’yan Majalisar Tarayya 8, da kuma Shugabannin Ƙananan Hukumomi 44 na Jihar Kano.

 

 

A nasa ɓangaren, Sakataren Jam’iyyar NNPP na Mazabar Diso-Chiranchi, Hon. Kabiru Zubairu, ya tabbatar da karɓar wasiƙar murabus ɗin, inda ya yaba wa Gwamnan bisa ayyukan ci gaba da ya gudanar a fannoni daban-daban da suka haɗa da ababen more rayuwa, ilimi, kiwon lafiya, da bunƙasa tattalin arziki.

Related Articles

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Back to top button