Gwamna Abba Kabir Yusuf Ya Yaba Wa Rundunar ‘yan Sandan jihar Kano

Gwamnan, wanda ya kai ziyarar a Hedikwatar ‘Yan Sanda ta Bompai a ranar 21 ga watan Janairun 2026, ya bayyana farin cikinsa musamman kan yadda ‘yan sandan suka yi gaggawar kama waɗanda ake zargi da kashe wata mata da ‘ya’yanta shida.
Gwamna Yusuf ya bayyana mamakinsa da jin daɗinsa kan yadda ‘yan sandan suka gudanar da bincike cikin gaggawa. Ya ce: “Lokacin da na ji labarin mummunan lamarin, na kira ka kuma na shawarce ka da ka tabbatar an kama waɗanda ake zargin cikin sa’o’i 12, amma abin mamaki, kun kama su cikin sa’o’i 6 kacal! Har ma ka haɗa ni da waɗanda ake zargin, da kuma mijin da mahaifin waɗanda abin ya faru da su.”
Ya kuma bayyana cewa ya samu damar sanar da Shugaban Ƙasa, Bola Ahmed Tinubu, game da wannan gagarumin kokari na ‘yan sanda, inda Shugaban Ƙasar ya nuna farin cikinsa.
Gwamnan ya bayyana cewa babban ƙalubalen da ya fuskanta tun bayan rantsar da shi a shekarar 2023 shi ne matsalar tsaro, musamman ta ‘yan daba, amma a yanzu an samu raguwar ayyukan ‘yan daba da kashi 70% a ƙarƙashin jagorancin CP Bakori.
Ya jaddada cewa bambancin siyasa bai kamata ya haifar da rarrabuwa ba, musamman a fannin tsaro.
Gwamna Yusuf ya ce ziyarar tasa na da nufin ƙarfafa haɗin gwiwa da fahimtar juna tsakanin Gwamnatin Jihar Kano da Rundunar ‘Yan Sanda.
Ya kuma yi alƙawarin ƙara tallafi ga ‘yan sanda, yana mai cewa: “Zaku ga canje-canje ta fuskar tallafin da zai zo muku.”
A nasa jawabin, Kwamishinan ‘Yan Sanda, CP Ibrahim Adamu Bakori, ya bayyana cewa ziyarar Gwamnan shaida ce ta ƙaunarsa ga ‘Yan Sandan Najeriya. Ya ce tun lokacin da ya karɓi ragamar aiki, goyon bayan Gwamnan da shawarwarinsa sun taimaka matuƙa wajen samun nasara a yaƙi da laifuka.
Ya kuma yaba wa al’ummar Kano kan yadda suke ba da haɗin kai wajen samar da bayanai, yana mai cewa ziyarar Gwamnan ta ƙara musu kwarin gwiwa.




