Siyasa

Atiku Ya yi Maraba da Komawar Peter Obi ADC

Tsohon ɗan takarar shugabancin kasarnan a jam’iyyar PDP, Atiku Abubakar, ya ce yana maraba da komawar tsohon ɗan takarar jam’iyyar Labour, Peter Obi, cikin jam’iyyar haɗaka ta ADC.

 

Atiku ya bayyana hakan ne a shafukan sada zumunta, inda ya ce matakin Obi na da muhimmanci wajen ƙarfafa haɗakar da ke da burin ƙalubalantar jam’iyya mai mulki da kuma samar da mulki nagari a Najeriya.

 

Ya ƙara da cewa yana fatan komawar Obi za ta buɗe ƙofa ga sauran ‘yan siyasar da ke da kishin ƙasa domin haɗa kai wajen kawo ci gaba da zaman lafiya.

Related Articles

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Back to top button