Kungiyar lauyoyin ta jihar kano ta yana da matakin da gwamnan kano ya dauka kan Wani kwamishina

Kungiyar Lauyoyi ta Najeriya (NBA), reshen
Ungogo, karkashin jagorancin Shugabanta, Ahmad Abubakar Gwadabe, Esq., na mika godiya da yabo ga Mai Girma Gwamnan Jihar Kano, Alhaji Abba Kabir Yusuf, bisa daukar mataki da gaggawa na kafa kwamitin bincike domin duba zargin da ake yi cewa wani jami’in gwamnati mai ci yanzu ya tsaya wa wani da ake zargi da safarar miyagun kwayoyi — wanda ke fuskantar shari’a a gaban Babbar Kotun Tarayya da ke Kano.
NBA reshen Ungogo na kallon wannan lamari da matukar damuwa, kasancewar laifukan da suka shafi safarar miyagun kwayoyi suna da nasaba da hauhawar matsalolin tsaro, lalacewar tarbiyyar matasa da kuma yawaitar munanan dabi’u a cikin al’umma. Laifukan da suka shafi miyagun kwayoyi suna haifar da tashin hankali, barazana ga lafiyar jama’a, tare da lalata ginshikin kyawawan dabi’un da al’umma ke da su.
Duk da cewa muna yaba da kafa wannan kwamitin bincike, muna kuma kira da karfi ga Gwamnatin Jihar da ta tabbatar da cewa rahoton kwamitin ya kasance a fili don tabbatar da gaskiya da rikon amana. Muna kuma bukatar mambobin kwamitin da su gudanar da aikinsu cikin cikakken gaskiya, kwararru, da rashin son zuciya — duk da cewa ba a bayyana a bainar jama’a sharuddan aikinsu ba tukuna.
NBA reshen Ungogo na nan daram wajen tsayawa don adalci, gaskiya a cikin mulki, da kuma kare muradun jama’a. Za mu ci gaba da mara baya ga duk wani yunkuri da ke neman kare doka da oda da kuma kare jiharmu daga mummunan tasirin shan miyagun kwayoyi da hadin baki da masu laifi.




