Labarai

An Kama Dan Jaridar Jamus a Turkiyya Bisa Zargin Yaɗa Ƙarya da Zagin Shugaba

Ofishin Babban Mai Gabatar da Ƙara na Istanbul ya bayyana cewa an kama ɗan jaridar, Alican Uludag, ne bisa wasu rubuce-rubucensa a kafafen sada zumunta.

An ce za a gurfanar da shi a gaban masu gabatar da ƙara domin ci gaba da bincike.

DW ta tabbatar da cewa an kama Uludag a Ankara sannan aka kai shi ofishin ‘yan sanda a Istanbul.

Haka kuma an gudanar da bincike a gidansa inda aka ƙwace wasu kayan aikin fasaha.

Babbar Daraktar DW, Barbara Massing, ta bayyana

zarge-zargen a matsayin marasa tushe, tana mai cewa kama ɗan jaridar wani yunƙuri ne na tsoratarwa da kuma nuna yadda gwamnati ke tauye ‘yancin ‘yan jarida.

A cewar DW, zarge-zargen na da alaƙa da wani rubutu da Uludag ya yi a dandalin sada zumunta na X kimanin shekara da rabi da ta gabata, inda ya soki matakan gwamnatin Turkiyya da suka kai ga sakin wasu da ake zargi ‘yan kungiyar ISIS ne.

Related Articles

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Back to top button