Ketare

Fiye da ƙungiyoyi 130 na jinƙai da sauran ƙungiyoyin fararen hula sun bukaci a gaggauta kawo ƙarshen ƙungiyar agaji ta Gaza (GHF), wani shiri na agaji da Isra’ila da Amurka ke marawa baya, suna mai cewa shirin ya zama barazana ga rayukan fararen hula.

A cewar ƙungiyoyin, fiye da Falasdinawa 500 ne suka mutu tun bayan da ƙugiyar agajin ta fara aiki a ƙarshen watan Mayu, bayan Isra’ila ta ƙulle Gaza na tsawon watanni uku.

Hakazalika, kimanin 4,000 ne suka jikkata yayin da suke ƙoƙarin karɓar agaji.

Ƙungiyoyin da suka haɗa da Oxfam da Save the Children da Amnesty International, da dai sauran su sun zargi dakarun Isra’ila da wasu ‘yan bindiga da buɗe wuta a kai a kai kan mutanen yayin da suka jira karɓan agaji.

Isra’ila ta musanta zargin cewa sojojinta na harbin masu karɓar agaji da gangan, tana mai cewa tsarin ƙungiyar agajin yana bai wa jama’a taimako kai tsaye ba tare da tsoma bakin Hamas ba.

Related Articles

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Back to top button