Ketare
Rundunar sojin kare ƙasar Uganda (UPDF) ta bayyana cewa sojoji biyar sun mutu yayin da jirgin su na Mi-24 da ke kan aikin kai wa sojojin Tarayyar Afrika kariya a Somaliya ya yi hatsari a babban filin jirgin saman Mogadishu jiya.

Rundunar ta sanar a shafinta na X cewa abubuwan fashewa da ke cikin jirgin sun fashe, wanda hakan ya jikkata wasu fararen hula uku tare da lalata gine-gine a kusa.
Gwamnatin tarayya ta Somalia ta aika da gaisuwar ta’aziyya ga gwamnatin Uganda.
A ranar 3 ga Yuni ne dai ƙungiyar al-Shabab ta bayyana cewa sun harbo jirgin sojojin ƙungiyar Tarayyar Afirka ɗin a yankin Shabelle ta tsakiya, amma ƙungiyar AU ta musanta wannan iƙirari inda ta ce hatsarin ya faru ne sakamakon matsalar fasaha.



