Labarai

Mataimakin Shugaban Majalisar Dattawa, Sanata Barau I. Jibrin, ya nesanta kansa daga wata kungiya da take fafutukar ganin Shugaban Kasa Bola Tinubu ya dauke shi a matsayin mataimakinsa a 2027.

Mai magana da yawun Sanatan, Isma’il Mudashir ne ya bayyana hakan a cikin wata sanarwa ranar Talata, inda ya ce a maimakon haka, kamata ya yi kungiyar ta fi mayar da hankali wajen mara wa Tinubu baya ya samu nasarar yunkurinsa na bunkasa Najeriya.

A kwanan nan ne dai wata kungiya mai suna Zauren Matasan APC na Arewacin Najeriya (NNPYA) ta ayyana goyon bayanta ga Tinubu ya dauki Sanatan a matsayin wanda za su yi takara tare.

Hakan dai ya biyo bayan jita-jitar da ake ta yadawa a ’yan kwanakin nan cewa ba lallai ne Tinubun ya sake yin takara tare da Kashim Shettima a matsayin mataimakinsa a 2027 din ba.

Related Articles

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Back to top button