Labarai

Tsohon Ministan Shari’a, Abubakar Malami, ya ce jam’iyyar ADC da yake ciki yanzu ta shirya tsaf domin fuskantar jam’iyyar APC mai mulki.

Ya ce wannan yunƙuri na neman kawo sauyi ne saboda irin halin da ake ciki a ƙasar.

Malami, wanda ya riƙe muƙamin minista a lokacin tsohon shugaban ƙasa Muhammadu Buhari, ya bayyana cewa gwamnatin Bola Ahmed Tinubu ta jefa talakawa cikin mawuyacin hali da ƙunci wanda ba za a iya misalta shi ba.

A hirarsa da BBC, Malami ya ce sun fito fili domin su ƙalubalanci gwamnati mai ci saboda yadda abubuwa suka taɓarɓare, musamman ɓangaren tsaro da tattalin arziƙi, da sauran matsalolin da ke addabar al’umma.

Related Articles

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Back to top button