Gwamnatin Kano Ta kafa kwamitin wayar da kan jama’a kan Rajistar Zaɓe

Gwamnatin Jihar Kano ta ƙara ƙaimi wajen wayar da kan al’umma domin ƙara yawan masu rajistar zaɓe, inda ta sanya burin rajistar sabbin masu kaɗa ƙuri’a miliyan huɗu a dukkan ƙananan hukumomi 44 kafin zaɓen 2027.
Kwamishinan Yaɗa Labarai da Harkokin Cikin Gida, Kwamared Ibrahim Abdullahi Waiya, ya bayyana cewa daga watan Agustan 2025 zuwa yanzu, mutane 267,790 sun kammala rajistar zaɓe kuma suna jiran karɓar katin zaɓensu (PVC).
Ya ce gwamnatin jihar ta kafa kwamitin wayar da kai mai ƙarfi domin ƙarfafa rajistar zaɓe da karɓar PVC, wanda ke da wakilan ma’aikatu da ƙungiyoyi daban-daban, tare da nufin kai saƙo zuwa dukkan ƙananan hukumomi.
Kwamared Waiya ya kuma bayyana cewa gwamnati na aiwatar da sama da ayyuka 900 a faɗin jihar, inda ya buƙaci al’ummar Kano su ci gaba da marawa gwamnati baya domin ci gaban dimokuraɗiyya da walwalar jama’a.


