Labarai

Wata sabuwa: wani sabon rikice ya barke a jam’iyar Labour

Sabon rikici ya sake kunno kai a cikin jam’iyyar Labour bayan da shugabancin jam’iyyar bangare Julius Abure, ya bai wa ɗan takararta na shugaban ƙasa a zaɓen 2023, Peter Obi, wa’adin awanni 48 ya yi murabus daga jam’iyyar, sakamakon shiga sabuwar haɗakar jam’iyyun adawa da aka ƙaddamar a Abuja.

Jam’iyyar ta bayar da wannan wa’adi ne a ranar Alhamis, kwana guda bayan Obi ya bayyana tare da wasu fitattun shugabannin adawa a wajen ƙaddamar da sabuwar haɗaka karkashin jam’iyyar African Democratic Congress (ADC).

Wannan haɗaka ta sabuwar jam’iyya na da nufin kalubalantar gwamnati mai ci a zaɓen shekarar 2027, kuma ta ɗauki jam’iyyar ADC a matsayin dandalinta na siyasa.

Amma sabanin tsofaffin ministoci Rotimi Amaechi da Abubakar Malami waɗanda suka fice daga jam’iyyar APC kafin shiga ADC, Peter Obi bai bayyana ficewarsa daga jam’iyyar Labour a hukumance ba duk da kasancewarsa cikin wannan sabon haɗin gwiwa.

A wata sanarwa da kakakin jam’iyyar Labour, Obiora Ifoh, ya fitar, jam’iyyar ta nesanta kanta daga haɗakar, inda ta siffanta ta a matsayin ƙungiyar ‘yan siyasar da suke neman mafitar kansu.

Related Articles

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Back to top button