Ketare

Hukumomin Hadaddiyar Daular Larabawa (UAE) sun gindaya wasu tsauraran sharudda ga ‘yan Najeriya da ke ziyartar birnin Dubai duk da cewa yanzu sun haramta bayar da bizar tsayawa na wucin gadi a birnin. 

Rahotanni sun bayana cewar tuni aka sanar da sabon umarnin ga kamfanonin shirya tafiye tafiye.

A wani babban cigaban da ake sa ran zai rage zirga-zirga daga Najeriya zuwa Dubai, kasar Hadaddiyar Daular Larabawa da ke kan gaba wajen kasuwanci da yawon bude ido tace duk wani dan Najeriya dake tsakanin shekaru 18 zuwa 45 an hana shi samun bizar yawon bude ido sai dai idan yana da dan rakiya.

Wannan dai na zuwa ne kusan shekara guda bayan da Hadaddiyar Daular Larabawa da Najeriya suka warware dokar hana shiga kasar na tsawon shekaru biyu da mahukuntan kasar suka yi wa ‘yan Najeriya.

Sai dai har yanzu dage haramcin ya zo ne da wasu tsauraran sharuddan da suka takaita yawan ‘yan Najeriya da ke balaguro zuwa Hadaddiyar Daular ta Larabawa.

Related Articles

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Back to top button