Gwamna Abba Yusuf Ya Sake Tsayar da Ranar Sauya Sheka Zuwa APC

Gwamnan Jihar Kano, Abba Kabir Yusuf, ya sake tsayar da wata rana domin sauya sheka daga jam’iyyar NNPP zuwa jam’iyya mai mulki ta APC, bayan dagewa da aka yi a lokuta da dama.
Majiyoyi sun bayyana cewa gwamnan ya sanar da hakan ne a wani taron sirri da ya yi da mambobin Majalisar Dokokin Jihar Kano a daren Alhamis.
A cewar majiyar, an tsayar da Asabar a matsayin ranar ficewarsa daga NNPP, Lahadi ranar bayyana shigarsa APC, yayin da Litinin za a karɓi katin zama mamba.
Rahotanni sun ce gwamnan ya cimma yarjejeniya da shugabancin APC na ƙasa kan samun kaso 60 cikin 100 na mukamai a jam’iyyar, tare da shirin kafa kwamiti da zai tsara dabarun samun rinjaye a babban taron jam’iyyar mai zuwa.
Dangane da Rabiu Musa Kwankwaso, Gwamna Yusuf ya ce ya gana da shugaban ƙasa ne domin shawo kan jagoran NNPP ya mara masa baya, sai dai majiyoyi sun nuna cewa Kwankwaso ba ya da niyyar shiga APC, sakamakon zurfafa tattaunawar haɗin gwiwa da Peter Obi na jam’iyyar Labour Party.




